Saturday, August 11, 2018


Matan kirki



Kalmar *"MACE"* tamkar *GOLD* ne
ko kuma muce  Sinadarin *ZINARI* mai yin *WALKIYA* a kowane *LOKACI*

       *MATA*
Sunada wani *SINADARI*na *FARIN JINI*  wanda yake da matukar Tasiri ga idon *MAZAJE*

       *MATA*
 Sunada matukar kima a Cikin
 Al'Ummah wadda har takai ga
 sun samu martaba da matsayi   Babbah.

       *MATA*
Sunada wani *LAUNI* mai Juya *MAZAJE* Tamkar Limzamin *DOKI*
komai *MATSAYINKA* *MULKI, KUƊI* ko *SARAUTA MACE* sai ta Juya ka.

       *MATA*
Sun Amsa Sunan Su *MATA* ga jan
*AJI*
 da Juyin Juya Hali, komai Rashin Kyan *MACE* Kalma daya Zata sa *KASO* ta nan Take.

       *MATA*
Sunada Hikima da Jurewa akan
abunda suke matukar *SO* amman sai sukasa Nunawa.

       *MATA*
Sunada Kunya, Hakuri da Juriya har sukan burgeka idan Ka Iya Zama
Dasu.

        *MATA*
Basu son mai kuntata masu koda
yaushe sunfi son Mai kyauta ta masu.

         *MATA*
Suna son *RAHA* da Abun *DARIYA*
ko kuma Nishadantarwa.

         *MATA*
Zuciyar su *FARA* ce tamkar farin
*RUWA* ba wuya shawo kansu idan
ransu ya Baci.

          *MATA*
Sunada *HAKURI* da Tausayi da kuma Firgita akan wani abu Kadan.

         *MATA*
Basa son, Saunan Mutum ko kuma ƙazamin Mutum.

         *MATA*
Sunfi son mai *BASU* ako wane Lokaci da kuma nuna Tausayi agare *SU.*

           *MATA*
Suna jajir cewa akan nuna *SOYAYYA* da Tausayin Junan.

           *MATA*
Sunfi son mutum mai *HAKURI* da
zafin naima har sukan yin Alfahari da Wannan.

           *MATA*
Sunada Yauqi da son *DAULA* da kuma Anunasu Manya ne.

*DARAJOJIN MATA GUDA (16) DA SUKA ƊARA MAZA! (USIKUM FIN NISA'I KAIRA)*
Inai muku wasicci da Alkairi ga
mata "Inji Manzon Allah {s.a.w} a cikin Huɗubar Ban Kwana"

*1- MACE CE*
   *TA FARA MUSULUNTA* a duk
duniya kuma ta yiwa musulunci hidima da dukiyar ta da duk abinda ta mallaka harda GwalaGwalanta *(NANA KHADIJA) (R.A)*

*2- MACE CE*
    Farkon wanda ta fara Istimbabi a cikin shari'ar musulunci........
*(NANA KHADIJA) (R.A)*

*3- MACE CE*
   Sanadiyyar samun Taimama a shari'a *(UMMUNA A'ISHA) R.A*

*4- MACE CE*
    Ta ilmantar da Sahabbai bayan wafatin Annabi{s.a.w}
 *NANA A'ISHA (R.a)*

*5- MACE CE*
   Sanadiyar tsiran sahabbai daga fushin Allah sanda akai sulhun
*HUDAIBIYYA* Kuma *MACE* ce ta shawo akan *SAHABBAI* har suka tsira daga  fushin Allah.
 *(UMMU SALAMA) R.A*

*6- MACE CE*
   Ta Kwantarwa Manzon Allah *HANKALI* Lokacin da Ifk ya faru a madina, kafin saukar wahayi
*(BARIRA) (R.A)*

*7- MACE CE*
    Wanda Manzon Allah *{S.A.W}* yace idan mutum ya tarbiyyantar da
ita koda bashi ya haife ta ba, zai shiga *ALJANNA* shi da Manzon Allah *{S.A.W}*

*8- MACE CE*
   Ta zamo Ma'auni damai Aure zai gwada kimarsa agun Mahaliccinsa, idan ya kyautata mata yanada sakamako mai kyau, idan kuma ya cuceta akwai uquba daga Allah.

*9- MACE CE*
   Shari'a ta tanadar *MATA* Ladan Jam'im Salloli guda biyar (5)
Da Juma'a da Jana'iza da Jihadi
duk basai taje ba,amma sanadiyyar ta Kyautatawa *MIJINTA* Allah Zai bata duk *LADAN* wadannan Ibadun.

*10- MACE CE*
    Sanadiyyar warware matsalar Zihari, suratul *(MUJADALA)*


*11- MACE CE*
      Ta fara yin Sa'ayi tsakanin *SAFA da MARWA (HAJARA)*

*12- MACE CE*
     Sanadiyyar tsiran mutanen sarauniyar Saba, suratl *(NAML)*
*BILKISU MAI GADON ZINARI*

*13- MACE CE*
    Sanadiyar musuluntar Sayyiduna Umar *(R.A) (FATIMA)*

*14-,MACE CE*
     Ake samun nutsuwa da ita! *LITASKUNU ILAIHA* Namiji bazai taba samun sukuni ba sai yana da mace!

*15- MACE CE*
      Duk mulkin mutum da dukiyar shi sai da ita yake kara kima a idon mutane! godiya nake.

*Mata iyayen mune Mugirmamasu!*

1 comment: